Filtrer par genre
- 448 - Gwamna Abba Yusuf ya mayar da Sarki Muhammadu Sunusi kan mukaminsa
Gwamnan Kano Abba Yusuf ya rattaba hannu a wata doka mai rusa ga baki daya masarautun Kano inda ya mayar da Sarki Muhammadu Sunusi kan mukaminsa.
Bashir Ibrahim Idris dangane da wannan mataki ya tattauna da Abdoulkarim Ibrahim da Nura Ado Suleiman a cikin shirin Duniyar mu a yau daga nan sashen hausa na Rfi.
Sat, 25 May 2024 - 447 - Bitar labaran mako: Bikin cika shekaru 17 da kafuwar Sashin Hausa na RFI
Daga cikin labarun da shirin na Muzagaya Duniya ya sake waiwaya akwai cikar Sashin Hausa na RFI shekaru 17 cif da kafuwa. Sai kuma matakin rushe sabbin masarautun da ya baiwa gwmna Abba Kabir Yusuf damar sake naɗa Sarki Muhammadu Sunusi na II a matsayin Sarkin Kano na 16.
A Guinea kuwa, gwamnatin sojin da ke jagorantar ƙasar ce ta rufe wasu kafafen yaɗa labarai da suka hada da gidan talabijin da kuma gidajen radio da dama.
Kotun Duniya ta baiwa Isra’ila Umarnin Dakatar da hare-haren da ta kaiwa a Rafah.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman.....
Sat, 25 May 2024 - 446 - Tattaunawa da Dr Kasim Garba Kurfi a shirin Duniyarmu a yauSun, 19 May 2024
- 445 - Mutane 15 ne suka rasa mutu sanadiyar harin da matashi ya kai Masallaci a Kano
Daga cikin labarun da shirin wannan makon ya ƙunsa akwai harin da wani matashi a Kano ya kaiwa Masallaci ta hanyar cinna masa wuta, wadda zuwa lokacin gabatar da wannan shiri aka tabbatar da salwantar rayukan mutane 15 daga cikin akalla 30 da ke cikin Masalacin. Shirin na kuma ɗauke da tattauna wa da tsohon gwamnan Jihar Jigawa Sule Lamiɗo, kan tuntubar junan da jiga-jigan jam’iyyun dawa suka fara yi a Najeriya, don kafa sabon ƙawancen da zai tunkari jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya.
Fira Ministan Senegal ya bayyana rashin gamsuwarsa kan wanzuwar sansanin sojojin Faransa a Ƙasar.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Nura Ado Suleiman.....
Sat, 18 May 2024 - 444 - Shirin ya duba zaben Chadi da kuma shirin ECOWAS na kafar rundunar yaki da ta'addanciSat, 11 May 2024
- 443 - Najeriya: Ƙarin albashi da gwamnati ta yi bai burge Ƙungiyar ƙwadago ba
Daga cikin batutuwan da shirin wannan lokaci ya waiwaya akwai, watsin da kungiyar kwadagon Najeriya ta yi da karin albashin ma’aikatan da gwamnatin kasar ta yi.
Sai kuma matakin Burkina faso na rufe karin kafafen yada labarai bisa rahoton da suka bayar na kisan fararen hula sama da 200 da sojoji suka yi.
A Kenya kuwa Ambaliyar ruwan ce ta lakume rayukan mutane da dama gami da raba wasu kusan dubu 200 da muhallansu.
Sat, 04 May 2024 - 442 - Hukumar EFCC na neman tsohon gwamnan jihar Kogi Yahya Bello ruwa a jallo
Daga cikin labarun da shirin karshen makon ya waiwaya akwai neman tsohon gwamnan jihar Kogi yahya Bello da hukumar EFCC ke yi ruwa a jallo, lamarin da ya kai ga daukar matakin dakile duk wani yunkurinsa na ficewa daga Najeriya
Shirin ya kuma leƙa gabas ta tsakiya inda Iran ta ƙi fusata kan makamai masu linzamin da na’urorin tsaron sararin samaniyarta suka kakkaɓo a birnin Isfahan, waɗanda wasu majiyoyi suka ce Isra’ila ce ta yi yunkurin kai mata hari da su.
Sat, 20 Apr 2024 - 441 - Muhimman labarun lamurran da suka wakana a makon da ya gabata
Masu sauraro daga sashin Hausa na RFI cikin shirin Mu Zagaya Duniya da saba zabo wasu daga cikin muhimman labarun lamurran da suka wakana a makon da ya gabata, domin bitarsu.
A ranar Larabar da ta gabata al'ummar Musulmin Najeriya suka bi sahun takwarorinsu na duniya wajen gudanar da Sallar Idi Karama, wadda aka saba gudanarwa bayan kammala azumin watan Ramadan.
Sat, 13 Apr 2024 - 440 - Karin kudin wutar lantarki ya fusata 'yan NajeriyaSat, 06 Apr 2024
- 439 - Bitar labaran mako: Yadda aka ceto daliban Kuriga a Kadunan Najeriya
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan mako tare da Rukayya Abba Kabara ya yi bitan wasu daga cikin labaran da suka fi daukar hankali a makon da ya wuce ciki har da labarin yadda gwamnatin Najeriya ta ceto daliban Kuriga da ke Jihar Kaduna tare da sada su da iyalan su.
Akwai dambarwar da ta zagaye batun karin kudin aikin hajji da ya gigita maniyyatan Najeriyar, sai dai kuma gwamnati ta kawo dauki a wasu jihohin.Zakuji yadda harin ta’addanci mafi muni a Rasha ya hallaka mutane sama da 130, kuma tuni wadanda aka kama suka amsa laifin su.
Sat, 30 Mar 2024 - 438 - Dubi akan matakin gwamnatin mulkin sojin Nijar na katse huldar aiki da dakarun Amurka
Daga cikin muhimman batutuwan da shirin ya waiwaya a wannan makon akwai matakin Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar na kawo karshen yarjejeniyar tsaro da ke tsakanin kasar da Amurka.
A Najeriya kuwa hukumar kare hakkin dan Adam ta kasar ce ta kawo karshen binciken da take gudanarwa kan zargin da ake yi wa rundunar sojin kasar na tilasta wa mata akalla dubu 10 zubar da juna biyun da suka samu a bisa tilas daga mayakan Boko haram
Sat, 23 Mar 2024 - 437 - Matakin Najeriya na bude iyakokin da ta rufe tsakaninta da Jamhutiyar Nijar
Daga cikin labarun da shirin ya kunsa a wannan makon, akwai matakin da Najeriya ta dauka na bude iyakokin da ta rufe tsakaninta da Jamhutiyar Nijar, tare da janye baki dayan takunkuman da ta kakaba mata.
Gwamnatin Birtaniya ta ce a shirye take ta baiwa ‘yan dubban ‘yan Rwanda da ke neman mafaka fam dubu uku kowannensu, to amma fa a bisa sharadin za su amince a mayar da su gida daga kasar ta Birtaniya
Sat, 16 Mar 2024 - 436 - Wasu daga cikin muhimman labarun da suka wakana a makon da ya gabata
Za a ji yadda aka sake zabar sabuwar ranar gudanar da zaben shugabancin kasar Senegal,Al’ummar Sudan ta Kudu sun tsallake rijiya da baya, domin kuwa aniyar wani sabon mugu da ya bayyana ce ta watse bayanda ya yi kokarin shirya juyin mulki a kasar, duk da cewar har yanzu basu gama murmurewa daga kazamin yakin basasar da ya tagayyara su ba, wato dai ana kukan targade karaya kuma na neman kunno kai.
Sat, 09 Mar 2024 - 435 - Wasu daga cikin muhiman labaren mako daga Rfi- Rikicin jihar Kano
Al’ummar Jihar Kano dake Najeriya sun tashi da labarin murabus din da shugaban hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya yi daga mukamin sa, sakamakon abinda ya kira sanyaya masa gwuiwar da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi, wajen sukar yadda suke gudanar da aikin su.
Wannan murabus din ta haifar da mahawara mai zafi a ciki da wajen jihar Kano, tare da hudubobi a Masallatan Juma’a dangane da muhimmancin hukumar da kuma rawar da take takawa.
Nasirudeen Muhammed zai jagoranci shirin.
Sat, 02 Mar 2024 - 434 - Jana'izar ma'aikacin RFI Hausa, Mahammane Salissou Hamissou a garin Tsibirin Gobir
A jiya Juma'a 17 ga watan Fabrairun 2024 ne aka gudanar da jana'izar ma'aikacin RFI Hausa, Mahammane Salissou Hamissou a garin Tsibirin Gobir, Mahammane Salissou Hamissou wanda Allah Ya yi wa rasuwa a ranar Larabar da ta gabata sakamakon hatsarin mota da ya rutsa da shi a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya.
Sat, 17 Feb 2024 - 433 - Matakin hadin gwiwar da Nijar ,Mali da Burkina Faso suka dauka, na sanar da ficewa daga ECOWAS
Daga cikin muhimman labarun makon jiya da shirin ya sake waiwaya domin bitarsu akwai, matakin hadin gwiwar da Nijar da Mali da kuma Burkina Faso suka dauka, na sanar da ficewa daga kungiyar ECOWAS.
Sai kuma sake karya darajar Naira da gwamnatin Najeriya ta yi, karo na biyu cikin watanni 8.
A Turai kuwa, za a ji yadda zanga-zangar manoma ta bazu zuwa sassan nahiyar saboda adawa da wasu sauye-sauyen mahukuntan kasashen yankin da suka ce ba za su lamunta ba.
Sat, 03 Feb 2024 - 432 - Taron Shugabannin arewacin Najeriya don lalubo hanyar magance matsalar tsaronSat, 27 Jan 2024
- 431 - Rikici tsakanin 'yan ta'adda a arewacin Najeriya ya illata bangaren Dogo Gide
Shirin wannan makon zai fara ne da waiwayar bata-kashin da aka yi tsakanin ‘yan bindiga a Najeriya, lamarin da ya kai ga illata bangaren daya daga cikin jagoran ‘yan ta’adddan da ya addabi jama’a.
Fira Ministan Jamhuriyar Nijar ya yi tatttaki zuwa Iran, bayan ganawarsa da mahukuntan kasar Rasha inda suka karfafa yarjejeniyar tsaron da suka kullla.
A gabashin Afirka kuwa cibi ne ya zama kari, domin kuwa gwamnatin sojin Sudan ce ta katse alaka da kungiyar kasashen yankin gabashin nahiyar ta Afirka, saboda gayyatar shugaba kuma Janar Abdel Fattah al-Burhan da suka yi.
Sat, 20 Jan 2024 - 430 - Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da nasarar Abba Gida-Gida a zaben gwamnan Kano
Cikin shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan makon tare da Nura Ado Suleiman, ya fara ne daga Kano a Najeriya, inda a ranar Juma’ar da ta gabata, kotun koli ta tabbatar da gwamna Abba Kabir Yusuf Abba na jam’iyyar NNPP a matsayin halastaccen gwamnan jihar.
Shirin ya kuma sake waiwayar matakin jagoran mulkin Sojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan na gindaya sharudda gabanin amincewa da shiga tattaunawa da bangaren jagoran dakarun RSF Mohamed Hamdan Dagalo da suka shafe fiye da watanni 9 suna gwabza yaki.
Mon, 15 Jan 2024 - 429 - Gwamnatin Najeriya ta haramta karbar shaidar karatun digiri daga Benin da Togo
Daga cikin labarun da shirin 'Mu Zagaya Duniya' ya sake waiwaya a wannan makon akwai matakin da gwamnatin Najeriya ta dauka na haramta karbar takardun shaidar kammala karatun digiri daga jami'o'in Jamhuriyar Benin da kuma kasar Togo.
Shirin ya kuma leka yankin Gabas ta Tsakiya, inda aka kashe kusan mutane 100 a wani harin ta'addanci da aka kai a kasar Iran.
Mon, 15 Jan 2024 - 428 - Bitar wasu muhimman labaran da suka faru a duniya cikin wannan mako
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai batun yadda yan ta'adda a Najeriya ke gina ramu suna boyewa, saboda barin wutar da suke sha daga sojojin kasar, sai kuma batun kammala ficewar sojojin Faransa a Nijer da dai sauran manyan labaran da suka hada da Burkina Faso, jamhuriyar Benin, yakin Isra'ila da Hamas, tare da dokar yan ci rani da Faransa ta amince da ita.
Sat, 23 Dec 2023 - 427 - ECOWAS/CEDEAO ta tabbatar da juyin mulki aka yi a Nijar
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai matakin da kungiyar kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ko CEDAEO ta dauka na amincewa da da cewar an yi juyin Mulki a Nijar, sannan kuma ta dakatar da ita daga cikin ta har sai lokacin da sojoji suka maida wa farar hula Mulki.
A Najeriya kuma, Bankin Duniya ne ya bukaci gwamnatin kasar ta fadada tsauraran matakan da take dauka na yi wa tattalin arzikin kasar garambawul, domin ceto shi daga durkushewa baki daya a nan gaba.
Sat, 16 Dec 2023 - 426 - COP28 - An samar da asusun tallafa wa kasashe don yaki da matsalar sauyin yanayi
Shirin "Mu zagaya duniya" na wannan makon tare da Khamis Saleh ya waiwari babban taron sauyin yanayi na COP28 da aka faro a Dubai, inda aka samar da wani asusu na musamman da manyan kasashe za su rinka zuba kudi don taimaka kananan kasashen da matsalar da ba su suka samar ba ta fi shafa.
Haka nan shirin ya kuma duba matakin da gwamnatin sojin Nijar ta dauka na dakatar da dokar hana safaran bakin haure, matakin da EU ke ganin a matsayin wata barazana ta kara yawan bakin hauren da zasu kwarara kasashenta.
Ku latsa a lamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh......
Sat, 02 Dec 2023 - 425 - Bitar wasu daga cikin labaran da suka dauki hankali na mako
Shirin zai kuma waiwayi kalaman da tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo yayi kan cewa Dimokaradiyar kasashen yammacin turai fa ba ta haifa wa nahiyar Afirka da mai idanu ba.
Cikin makon da ya gabata, aka shiga rudani, yayin da kuma a gefe guda aka yi ta tafka muhawara a Kano dake arewacin Najeriya, bayan da kotun daukaka kara ta fitar da takardar hukuncin da ta yanke kan shari’ar zaben gwamnan jihar a juma’ar waccan makon da ya gabata, inda ta tabbatar da hukuncin kotun sauraren kararrakin zabe.
Sai ku biyo mu..............
Sat, 25 Nov 2023
Podcasts similaires à Mu Zagaya Duniya
- Conversations ABC listen
- El Partidazo de COPE COPE
- Herrera en COPE COPE
- The Dan Bongino Show Cumulus Podcast Network | Dan Bongino
- Es la Mañana de Federico esRadio
- La Noche de Dieter esRadio
- Dateline NBC NBC News
- 財經一路發 News98
- Más de uno OndaCero
- La Zanzara Radio 24
- L'Heure Du Crime RTL
- El Larguero SER Podcast
- Nadie Sabe Nada SER Podcast
- SER Historia SER Podcast
- Todo Concostrina SER Podcast
- 安住紳一郎の日曜天国 TBS RADIO
- TED Talks Daily TED
- アンガールズのジャンピン[オールナイトニッポンPODCAST] ニッポン放送
- 辛坊治郎 ズーム そこまで言うか! ニッポン放送
- 飯田浩司のOK! Cozy up! Podcast ニッポン放送
- 吳淡如人生實用商學院 吳淡如
- 武田鉄矢・今朝の三枚おろし 文化放送PodcastQR
Autres podcasts de Actualités et Politique
- Les Grosses Têtes RTL
- Hondelatte Raconte - Christophe Hondelatte Europe 1
- L'œil de Philippe Caverivière RTL
- C dans l'air France Télévisions
- Laurent Gerra RTL
- Enquêtes criminelles RTL
- Bercoff dans tous ses états Sud Radio
- Hondelatte Raconte - Cote B Europe 1
- L’heure du crime : les archives de Jacques Pradel RTL
- Global News Podcast BBC World Service
- Les récits de Stéphane Bern Europe 1
- LEGEND Guillaume Pley
- L'Heure des Pros CNEWS
- Apolline Matin RMC
- Lenglet-Co and You RTL
- RTL Matin RTL
- Pascal Praud et vous Europe 1
- L'invité politique Sud Radio Sud Radio
- Gaspard Proust - Les signatures d'Europe 1 Europe 1
- C ce soir France Télévisions