Podcasts by Category
- 579 - Nazari kan yadda wasannin kwata finals na gasar zakarun Turai su ka gudana
Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon ya maida hankali ne kan yadda wasannin matakin kwata finals na gasar zakarun Turai su ka gudana. A makon da ya gabata ne dai aka kammala wasannin zagayen, inda aka fafata a wasanni 4. Dortmund da aris Saint-Germain da Bayern Munich da Real Madrid ne suka kaiga wasan kusa da na karshe a gasar ta bana.
A yanzu Bayern Munich zata fafata da Real Madrid ita kuwa Borussia Dortmund ta kara Paris Saint-Germain.
Ku letsa alamar sauti don jin cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Mon, 22 Apr 2024 - 578 - Hasashen yadda za ta kaya a gasar Firimiyar Ingila
Shirin a wannan lokaci ya fi karkata akalar ne kan gasar Firimiyar Ingila, wadda ke ci gaba da jan hankali, duk da shawo gangarar da akayi.
Yar manuniyar dai tuni ta fada kan kungiyoyin ukun saman tebur, wato Manchester City, Arsenal da Liverpool, lura da yadda suke kan kan kan a yawan maki, abunda ke kara nunawa duniya yadda gasar ta Firimiya ta ke ci gaba da jan zarenta a fagen tamola.
Ko da yake a halin yanzu Manchester City ce ta karbe ragamar teburin wannan gasa, bayan rashin nasarar da Arsenal da kuma Liverpool suka samu a nasu wasannin.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Khamsi Saleh.
Mon, 15 Apr 2024 - 577 - Shiri na musamman kan shirye-shiryen gasar Olympics kashi na 2
A wannan makon Shirin Duniyar Wasanni ya yi duba ne kan yadda ake tufka da warwara game da tsarin tsaro a lokacin gasar wasannin motsa jiki ta Olympics da birnin Paris zai karbi bakunci a watan Yulin wannan shekarar.
Shire-shiryen gudanar da gasar wasannin motsa jiki ta Olympics da birnin Paris na Faransa zai karbi bakunci a watan Yuli mai zuwa sunyi nisa, domin dai rahotanni na nuna cewar an kammala tanadin kusan dukkanin inda za a gudanar da wadannan wasanni.
Sai dai wani hanzari ba guda ba, duk da matakan da kasar ta Faransa ta dauka na tabbatar da tsaron ‘yan wasa da kuma na ‘yan kallo, bayanai na nuna cewar akwai alamun fuskantar barazanar tsaro a lokacin gasar.
Wannan lamari dai ya biyo bayan harin ta’addancin da aka kai birnin Moscow wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane akalla 140.
A lokacin wata zantawa da aka yi shugaban Faransa Emmanuel Macron a makon da ya gabata, ya ce babu shakka, akwai yuwuwar Rasha za ta kai hari a lokacin gasar da ke tafe.
Kai hari a lokacin gasar Olympics
Kai hari a yayi gasar gujeguje da tsalle-tsalle ta Olympics a iya cewa ba sabon abu bane, domin a baya an sha samun irin hakan, wanda aka kai a shekarar 1972 a Munich da kuma a shekarar 1996 a Atlanta.
Duk da cewa a cikin watan da ya gabata ministar Wasannin Faransa Amelie Oudea-Castera, ta ce a yanzu babu wata barazanar hare-haren ta’addanci da gasar gujeguje da tsalle-tsalle ta Olympics ke fuskanta, sai dai wasu da dama na cewa barazanar abu ne da ke da alaka da rikicin da ake gwabzawa tsakanin Rasha da Ukraine da ya kwashe sama da shekaru biyu anayi, wanda kasashen duniya ciki harda Faransa ke goyonma Ukraine baya domin fafatawa da Rasha.
Yadda gasar Olympics ke samar da hadin kai
Ita dai wannan gasa ana ganinta a matsayin wata farfajiya ta samar da hadin kai, ganin yadda take hada dukkanin bangarorin duniya waje guda.
Domin idan aka koma baya cikin tarihi, bayan kawo karshen yakin duniya na biyu, gasar da aka gudanar ta shekarar 1952, ta kasance taron wasanni mafi girma a duniya da aka gudanar.
Ƴan wasa dubu 4 da dari 955 ne suka halarci gasar daga kasashe 69, bayan maido da kasashen Japan da Jamus da wasu kasashe 13 da a karon farko ke nan suka halarci gasar, cikinsu har da Isra’ila wacce ta kasance sabuwar kasar da aka kirkira da ta samu amincewar Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 1948, da Vietnam da ke cikin rudanin siyasa.
To sai dai ana ganin cewa a wannan karon siyasa ta shiga cikin lamarin wanda ke kokarin kawo rarrabuwar kai.
Martanin Rasha game da zargin kai hari
To sai dai a wani martani da Rasha ta maida game da kalaman Macron ta bakin mai magana da yawun fadar shugaban kasar Dmitry Peskov, ta ce zargin na Macron babu tushe a cikinsa kuma wani matakine na yada labaran kanzon kurege da kasashen yammaci ke yiwa Rasha.
Mon, 08 Apr 2024 - 576 - Sharhi game da kamun ludayin Finidi George a tawagar Super Eagles
Shirin a wannan mako shirin ya yi sharhi ne kan kamun ludayin mai rikon kwaryar tawagar Super Eagles ta Najeriya Finidi George, bayan da tawagar ta buga wasannin sada zumunci biyu a makon daya gabata karkashin kulawar Finidi George da aka damkawa tawagar a hannunsa a matsain mai horaswa na rikon kwarya.
Tawagar ta yi nasara kan takwararta ta Ghana a wasan farko da tayi, sai dai kuma ta sha kashi a hannun Mali karo na farko cikin gwamman shekaru da hakan ta faru.
Ku latsa alamar sauti donjin cikakken shirin tare da Khamis Saleh......
Mon, 01 Apr 2024 - 575 - Masar ce ta daya a gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Afrika da aka yi a Ghana
Shirin Duniyar Wasanni a wannan mako yayi duba ne kan yadda gasar guje-guje da tsalle -tsalle ta nahiyar Afrika ta gudana a kasar Ghana. Kasar Masar ce ta zamo zakarar lashe lambobin yabo har 189, sai Najeriya da ke bi mata da lambobn yabo 120, yayinda Janhuriyar Nijar ta lashe lambobin yabo 11, lamarin da ya bata damar zama amatsayi na 16 a teburin kasashe 53 da suka halarci gasar bayan da Cape Verde ta janye daga fafatawa a wannan karon.
Wannan ne kuma karo na 13 da ake gudanar da wannan gasa a tarihi, inda aka gudanar da wasanni kusan 30.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.....
Mon, 25 Mar 2024 - 574 - Sharhi kan yadda wasannin kwata finals na gasar zakarun Turai za su gudana
Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon ya maida hankali ne kan yadda wasannin matakin kwata finals na gasar zakarun Turai za su gudana. A ranar Juma’ar da ta gabata ce dai hukumar kula da wasan kwallon kafar Turai UEFA ta hada yadda kungiyoyi 8 da suka yi saura a gasar zakarun Turai z asu kara da junanansu. Tsohon kyaftin din Najeriya wanda kuma ya taba lashe gasar da kungiyar Chelsea Mikel John Obi ne ya jagoranci hada yadda kungiyoyin za su kara da juna.
Arsenal za ta fafata da Bayern Munich, Atletico Madrid za ta kece raini da Borussia Dortmund, Real Madrid ta kara da Manchester City ya yin da Paris Saint-Germain za ta kara da Barcelona.
Ku letsa alamar sauti don jin cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Mon, 18 Mar 2024 - 573 - Ci gaban da aka samu a wasan damben gargajiya a NajeriyaMon, 11 Mar 2024
- 572 - Yadda aka kammala zangon farko na gasar kwallon kafa ta Firimiyar Najeriya
Shirin awanan lokaci zai nazari game da yadda zangon farko na gasar Firimiyar Najeriya ya kammala, inda tuni aka juya zagaye na biyu na gasar ta kwararru.
Shirin ya kuma duba batun soma gasar a kan lokaci da kuma batun daukar nauyi, sai kuma batun rashin ingancin filaye, baya ga kuma karanchin samun bayanan ‘yan wasan da ke taka leda a gasar.
Latsa alamar sauti don sauraron shirin:
Mon, 04 Mar 2024 - 571 - Nazari kan komawar Kylian Mbappe kungiyar Real Madrid a kaka mai zuwa
Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon ya yi nazari ne kan komawar dan wasan gaba na kungiyar PSG, Kylian Mbappe kungiyar Real Madrid a karshen kakar bana. Yanzu dai za a iya cewa an yi ta, ta kare bayan da a ranar 13 ga wannan watan ne dan wasan mai shekara 25 ya sanar da kungiyarsa PSG batun sauya shekarar tasa da zarar kwantiraginsa ya kare a karshen kakar watan Yuni.
Kungiyar Real Madrid dai tayi suna wajen dauko manyan ‘yan wasan da tauraruwarsu ke haskawa a fagen kwallon kafa a duniya, ba tare da la'akari da tsadarsu ba.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.....
Mon, 26 Feb 2024 - 570 - Yadda aka gudanar da gasar Polo ta bana a garin Jos
Shirin Duniyar Wasanni a wannan makon ya mai da hankali ne kan yadda aka gudanar da gasar Polo a Jahar Filato da ke arewacin Najeriya. A wannan karo, club club din wasan kwallon dawakin da suka fafata a gasar sun fito ne daga jihohin Lagos, Nasarawa, Bauchi, Taraba, Kaduna, Kano, Niger da kuma Katsina. A karshe dai club din Keffi Ponies ta jihar Nasarawa ta lashe gasar a karawar karshe da suka yi da Malconmines daga Filato mai masaukin baki.
Ku latsa alamar suti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh......
Mon, 19 Feb 2024 - 569 - Yadda Ivory Coast ta lashe kofin AFCON bayan ta doke Najeriya
A daren jiya Lahadi ne aka kammala gasar lashe kofin Afrika AFCON karo na 34 da Ivory Coast ta karbi baukunci kuma daga bisa ta lashe gasar. Najeriya ce ta fara zura kwallon farko ta hannun William Ekong tun kafin a tafi hutun rabin lokacin, sai dai bayan dawowa ne tawagar ta Elephants ta farke ta hannun Kesse kafin daga bisani a minti na 81 ta kara kwallo ta hannun Sebestin Hallar wacce ta bata nasara.
Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakken shirin tare da Khamis Saleh
Mon, 12 Feb 2024 - 568 - Mai masaukin baki Ivory Coast ta lashe kofin AFCON bayan doke Najeriya
Shirin Duniyar Wasanni tare da Khamis Saleh, ya mayar da hankali ne kan yadda ta kaya a wasan karshe na cin kofin AFCON wanda Ivory Coast mai masaukin baki ta lashe bayan doke Najeriya da kwallaye 2 da 1.
Shirin ya yi bitar muhimman batutuwan da ke kunshe a gasar a tsawon makwanni 3 da aka shafe ana fafatawa tsakanin kasashe 24.
Sai kuma batun tagomashin da kasashen da suka zo na daya da na biyu da kuma na 3 za su samu.
Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.....
Mon, 12 Feb 2024 - 567 - Yadda wasannin zagayen Kwata final suka kaya a gasar AFCON
Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan lokacin yayi nazari ne akan wasannin matakin dab da na kusa da na karshe wato na zagayen Kwata final da aka yi a gasar AFCON.
Yanzu haka dai kasashe hudu ne suka rage a gasar ta cin kofin kasashen nahiyar Afirka da kasar Ivory Coast ke karbar bakunci, bayan wasannin da aka fafata a ranakun Juma’a da Asabar.
Mon, 05 Feb 2024 - 566 - Matakin zagayen dab da na kusa da na karshe a gasar lashe kofin Afrika AFCON
A yau Juma’a nan ce dai za a fara buga wasannin zagen dab da na kusa da na karshe a gasar lashe kofin Afrika AFCON da ke gudana a kasar Ivory Coast.
Za kuma a fara karawar ne tsakanin Najeriya da Angola karfe shida agogon Najeriya, kafin da misalign karfe 9 a buga wasa tsakanin DR Congo da Guinea.
A wasannin gobe Asabar, akwai karawa tsakanin Mali da Cote d’Ivoire sai kuma Cape Verde da Afrika ta Kudu.
Fri, 02 Feb 2024 - 565 - Nazari kan karawar da aka yi tsakanin Najeriya da Kamaru a gasar AFCON 2023
A ranar asabar ne dai aka fafata tsakanin tawagar Super Eagels ta Najeriya ta tawkararta ta Indomitable Lions ta Kamaru, a wasan zagayen ‘yan 16 a gasar lashe kofin Afrika AFCON da Ivory Coast ke karbar bakunci.
Wannan wasa dai ya ja hankali a wannan gasa, ganin yadda kasashen biyu ke da suna a fagen kwallon kafar Afrika, sannan kuma akwai dadaddiyar hamayya a tsakaninsu.Mon, 29 Jan 2024 - 564 - Najeria da Kamaru za su fafata a zagaye na 2 na gasar AFCON
Najeriya karkashin mai horar da kungiyar Jose Peseiro za ta nemi kare maratabar ta da kuma neman ganin ta tsallaka mataki na gaba a wanan gangami,yayida a daya wajen ,Kamaru a cewar mai horar da ita ,Rigobert Song za su kasance a kan bakar su na ganin su doke Najeriya.
A tarihi,haduwar wadanan kungiyoyi Najeriya da Kamaru a shekaru baya suka kasance gagara badau a fagen tamola, Najeriya da Kamru sun hadu sau 22.,Najeriya ta samu nasara a wasanni 11 da ta buga da Kamaru. Yayin da Kamaru ta samu galaba a kan Najeriya sau hudu Kungiyoyin biyu sun yi canjaras sau bakwai.
A tarihin lashe kofin gasar Afirka na kwallon kafa baya ga Masar,da ta lashe Kofin sau 7,Kamaru ta daga wannan kofi sau 5 sai Ghana sau 4.
A bangaren Najeriya,kungiyar Super Eagles ta lashe kofin sau uku, shekarar 1980,1994 sai 2013..
Khamis Saley a cikin wannan shiri na Duniyar wasanni,ya mayar da hankali a gasar.
Fri, 26 Jan 2024 - 563 - Yadda kasashe ke bayar da mamaki a wasannin gasar AFCON a Ivory Coast
Shirin duniyar wasanni tare da Khamis Saleh ya mayar da hankali kan yadda gasar AFCON ke ci gaba da gudana a Ivory Coast, gasar da zuwa yanzu aka kammala zagaye biyu na matakin rukuni.
Gasar ta AFCON a bana ta zo da wani yanayi ta yadda kasashen da ba a tsammanin su iya kai labari ke ci gaba da bayar da mamaki, yayinda wasu manyan kasashe kuma a fagen tamaular nahiyar suka kasa katabus.
Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin..
Mon, 22 Jan 2024 - 562 - Yadda aka kammala wasannin farko na rukuni a gasar AFCON
Shirin "Duniyar Wasanni" a wannan lokaci zayyi duba ne akan yadda aka kammala wasannin farko na matakin rukuni da kuma yadda aka faro na biyu a gasar AFCON da ke gudana a Ivory Coast. An kuma fara wasannin ne da karawar da aka yi tsakanin Equatorial Guinea Guinea-Bissau, inda Equatorial Guinea ta samu nasara akan Guinea-Bissau da ci 4-2.
Sai kuma wasa na biyu da aka yi a rukunin na A tsakanin Najeriya da Ivory Coast mai masaukin baki, kuma kwallo daya mai ban haushi da zura tawagar Super Eagles ta Najeriya ta zura ta hannun William Troost-Ekong ce ta bada nasara a wasan.
Wannan nasara ta farko da Super Eagles ta samu a rukunin A, ta farfado da fatan Najeriya na kai wa zagaye na biyu a gasar lashe kofin Afrika, yayinda ita kuwa Ivory Coast hannun agogo ya koma mata baya.
Ku lastsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......
Fri, 19 Jan 2024 - 561 - Gasar cin kofin kasashen Afirka ta kankama a Ivory CoastMon, 15 Jan 2024
- 560 - Yadda aka daina bai wa matasan 'yan wasan Najeriya dama a Super Eagles
Shirin a wannan mako ya mayar da hankali ne ga batun yadda ake korafin rashin amfani da ‘yan wasan gida a tawagar babbar kungiyar kwallon kafa ta Najeriya.
Sabanin a baya, da hukumar kwallon kafa ta Najeriyar, kan shirya wasanni na musamman domin fitar da 'yan wasan da za ta yi amfani da su wajen wakiltar kasar a manyan wasanni.
Kan wannan kalubale ne Khamis Saleh ya tattauna da masana a fannin kwallon kafa.
Shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.
Fri, 29 Dec 2023 - 559 - Shiri na musamman a kan gasar Olympics
A yayin da wakilan kasashen ke kintsawa don zuwa gasar wasannin motsa jiki na Olympic da za a yi a birnin Paris na kasar Faransa a shekara mai zuwa, shirin 'Duniyar Wasanni', ya kawo tarihin gasar, inda ya yada zango a Najeriya, wadda tawagar kwallon kafarta ta 'Dream Team' ta kasance ta farko a nahiyaar Afrika da ta lashe kofin kwallon kafa a gasar Olympiic a shekarar1996.Shirin ya samu damar tattaaunawa da wasu 'yan wasa da jami'ai da aaka dama da su a lokacin.
TARIHIN GASAR WASANNI TA OLYMPIC
Gasar motsa jiki ta Olympics an fara gudanar da ita ne a karni na 8 a kasar Girka, sai dai daga bisani aka dakatar da ita.
Bayan dakatar da gasar na tsawon lokaci, a shekarar 1940, kwamitin shirya gasar Olympics na Duniya IOC ya zabi babban birnin kasar Finland Helsinki don gudanar da gasar, amma sai dai sanadiyar barkewar Yakin Duniya na 2 aka sake dakatar ita.
Bayan kawo karshen yakin, a shekara ta 1946, IOC ya yanke shawarar sake farfado da harkar wasannin Olympics na zamani, inda aka fara gudanar da wasannin gasar a shekarar 1948 a birnin London na kasar Ingila, duk da cewa itama ta kasance kamar sauran kasashen Turai, ta na cikin yanayi na matsi, amma sai da aka sake gina birnin na London don gudanar da gasar wasannin Olympics.
Fiye da 'yan wasa dubu 4 ne suka fafata a wasanni 136, sai dai ba a gayyaci kasashen Japan da Jamus ba, yayin da Tarayyar Soviet da aka gayyata ta kaurace wa gasar.
Shekaru hudu bayan waccan gasar, birnin Helsinki na kasar Finland ta karbar bakuncin gasar, da aka yi wa lakabi da “gasa ta zamani”.
An fara wasanni ne a ranar 19 ga Yuli zuwa 3 ga Agustan 1952, wannan gasa ta Olympics wacce ita ce karo na 15, ta kasance taron wasanni mafi girma a duniya da aka gudanar bayan kammala yakin duniya na biyu.
‘Yan wasa dubu 4 da dari 955 ne suka halarci gasar daga kasashe 69, bayan maido da kasashen Japan da Jamus da wasu kasashe 13 da a karon farko ke nan suka halarci gasar, cikinsu har da Isra’ila wacce ta kasance sabuwar kasar da aka kirkira da ta samu amincewar Majalisar Dinkin Duniya a shekarar 1948, da Vietnam da ke cikin rudanin siyasa.
Duk da cewar wannan gasar ba a farota da kasashen nahiyar Afrika ba, akwai wakilan nahiyar da suka shigo daga baya kuma suka nuna bajinta, musammanma a bangaren wasan kwallon kafa, inda a shekarar 1996 da kuma 2000 kasashen Najeriya da Kamaru suka taka rawar gani wajen lashe gasar.
A shekarar 1996 ce Najeriya ta kafa tarihin samun nasarar lashe lambar zinari a bangaren kwallon kafar gasar, lamarin daya kara karfafawa sauran kasashen nahiyar gwiwa.
A biyo mu a kashi na gaba don jin tagomashin da nahiyar Afrika ta samu a wannan gasa ta olympic.
Mon, 18 Dec 2023 - 558 - An gudanar da wassan karshe na gasar Dambe Warriors a jahar Kano
Shirin "Duniyar Wasanni" a wannan makon yayi duba ne kan yadda akayi karan battar karshe ta gasar Dambe Warriors, inda Dogon Sisco ya kasha Husaini Dan Saudiyya a wasan karshe na kasa da kasa. haka nan an kuma doka wasu wassani daban-daban inda 'yan wasa suka nuna bajintarsu.
A wasa tsakanin 'Yar Mage da Alaye, 'Yar Mage ne yayi nasara da makin kai naushi 89 da 82, abunda yasa ya lashe kyautar naira dubu dari biyar da damar shiga gasar Dambe Warriors ta shekarar 2024.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.....
Mon, 04 Dec 2023 - 557 - Yadda kwallon kafa ke bada gudunmuwa wajen samar da hadin kai a Najeriya
Shirin "Duniyar Wasanni" a wannan makon yayi duba ne kan yadda wani dan Arewacin Najeriya Alhaji Abdullahi Miko Nakeli, ya samar da kungiyar kwallon kafa ta Spatters football club a Jahar Lagos yankin Kudancin kasar, da ke baiwa matasa damar samun manyan kungiyoyi a ciki da wajen Najeriya.
Akwai ‘yan wasa da dama da suka fito daga arewacin Najeriya da ke wasa a wannan kungiyar, wacce ta ke baiwa ‘yan wasa daga yankin arewaci dama don nuna irin tasu kwarewa da kuma bajinta a wannan bangare.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh......
Mon, 27 Nov 2023 - 556 - Najeriya: Yadda aka gudanar da gasar kwallon Polo na 2023 a KadunaMon, 13 Nov 2023
Podcasts similar to Wasanni
- Global News Podcast BBC World Service
- El Partidazo de COPE COPE
- Herrera en COPE COPE
- The Dan Bongino Show Cumulus Podcast Network | Dan Bongino
- Es la Mañana de Federico esRadio
- La Noche de Dieter esRadio
- Hondelatte Raconte - Christophe Hondelatte Europe 1
- Curiosidades de la Historia National Geographic National Geographic España
- Dateline NBC NBC News
- 財經一路發 News98
- La rosa de los vientos OndaCero
- Más de uno OndaCero
- La Zanzara Radio 24
- L'Heure Du Crime RTL
- El Larguero SER Podcast
- Nadie Sabe Nada SER Podcast
- SER Historia SER Podcast
- Todo Concostrina SER Podcast
- 安住紳一郎の日曜天国 TBS RADIO
- アンガールズのジャンピン[オールナイトニッポンPODCAST] ニッポン放送
- 辛坊治郎 ズーム そこまで言うか! ニッポン放送
- 飯田浩司のOK! Cozy up! Podcast ニッポン放送
- 吳淡如人生實用商學院 吳淡如
- 武田鉄矢・今朝の三枚おろし 文化放送PodcastQR
Other Sports & Recreation Podcasts
- L'After Foot RMC
- Super Moscato Show RMC
- Rothen s'enflamme RMC
- Julien Cazarre RMC
- Les Grandes Gueules du Sport RMC
- On refait le match RTL
- Les Paris RMC RMC
- WINAMAX FOOTBALL CLUB Winamax
- RMC Poker Show RMC
- RMC Football Show RMC
- Basket Time RMC
- Stephen Time RMC
- Bartoli Time RMC
- Radio Radio Radio Radio
- After Marseille RMC
- Radio Foot Internationale RFI
- Radio Bichon Le podcast des passionnés du bâtiment
- Rothen Régale RMC
- Le Top de L'After foot RMC
- Japanimation Station's Kyoto Vacation Jonathan Lack & Sean Chapman