Podcasts by Category
- 442 - Hukumar EFCC na neman tsohon gwamnan jihar Kogi Yahya Bello ruwa a jallo
Daga cikin labarun da shirin karshen makon ya waiwaya akwai neman tsohon gwamnan jihar Kogi yahya Bello da hukumar EFCC ke yi ruwa a jallo, lamarin da ya kai ga daukar matakin dakile duk wani yunkurinsa na ficewa daga Najeriya
Shirin ya kuma leƙa gabas ta tsakiya inda Iran ta ƙi fusata kan makamai masu linzamin da na’urorin tsaron sararin samaniyarta suka kakkaɓo a birnin Isfahan, waɗanda wasu majiyoyi suka ce Isra’ila ce ta yi yunkurin kai mata hari da su.
Sat, 20 Apr 2024 - 441 - Muhimman labarun lamurran da suka wakana a makon da ya gabata
Masu sauraro daga sashin Hausa na RFI cikin shirin Mu Zagaya Duniya da saba zabo wasu daga cikin muhimman labarun lamurran da suka wakana a makon da ya gabata, domin bitarsu.
A ranar Larabar da ta gabata al'ummar Musulmin Najeriya suka bi sahun takwarorinsu na duniya wajen gudanar da Sallar Idi Karama, wadda aka saba gudanarwa bayan kammala azumin watan Ramadan.
Sat, 13 Apr 2024 - 440 - Karin kudin wutar lantarki ya fusata 'yan NajeriyaSat, 06 Apr 2024
- 439 - Bitar labaran mako: Yadda aka ceto daliban Kuriga a Kadunan Najeriya
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan mako tare da Rukayya Abba Kabara ya yi bitan wasu daga cikin labaran da suka fi daukar hankali a makon da ya wuce ciki har da labarin yadda gwamnatin Najeriya ta ceto daliban Kuriga da ke Jihar Kaduna tare da sada su da iyalan su.
Akwai dambarwar da ta zagaye batun karin kudin aikin hajji da ya gigita maniyyatan Najeriyar, sai dai kuma gwamnati ta kawo dauki a wasu jihohin.Zakuji yadda harin ta’addanci mafi muni a Rasha ya hallaka mutane sama da 130, kuma tuni wadanda aka kama suka amsa laifin su.
Sat, 30 Mar 2024 - 438 - Dubi akan matakin gwamnatin mulkin sojin Nijar na katse huldar aiki da dakarun Amurka
Daga cikin muhimman batutuwan da shirin ya waiwaya a wannan makon akwai matakin Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar na kawo karshen yarjejeniyar tsaro da ke tsakanin kasar da Amurka.
A Najeriya kuwa hukumar kare hakkin dan Adam ta kasar ce ta kawo karshen binciken da take gudanarwa kan zargin da ake yi wa rundunar sojin kasar na tilasta wa mata akalla dubu 10 zubar da juna biyun da suka samu a bisa tilas daga mayakan Boko haram
Sat, 23 Mar 2024 - 437 - Matakin Najeriya na bude iyakokin da ta rufe tsakaninta da Jamhutiyar Nijar
Daga cikin labarun da shirin ya kunsa a wannan makon, akwai matakin da Najeriya ta dauka na bude iyakokin da ta rufe tsakaninta da Jamhutiyar Nijar, tare da janye baki dayan takunkuman da ta kakaba mata.
Gwamnatin Birtaniya ta ce a shirye take ta baiwa ‘yan dubban ‘yan Rwanda da ke neman mafaka fam dubu uku kowannensu, to amma fa a bisa sharadin za su amince a mayar da su gida daga kasar ta Birtaniya
Sat, 16 Mar 2024 - 436 - Wasu daga cikin muhimman labarun da suka wakana a makon da ya gabata
Za a ji yadda aka sake zabar sabuwar ranar gudanar da zaben shugabancin kasar Senegal,Al’ummar Sudan ta Kudu sun tsallake rijiya da baya, domin kuwa aniyar wani sabon mugu da ya bayyana ce ta watse bayanda ya yi kokarin shirya juyin mulki a kasar, duk da cewar har yanzu basu gama murmurewa daga kazamin yakin basasar da ya tagayyara su ba, wato dai ana kukan targade karaya kuma na neman kunno kai.
Sat, 09 Mar 2024 - 435 - Wasu daga cikin muhiman labaren mako daga Rfi- Rikicin jihar Kano
Al’ummar Jihar Kano dake Najeriya sun tashi da labarin murabus din da shugaban hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya yi daga mukamin sa, sakamakon abinda ya kira sanyaya masa gwuiwar da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi, wajen sukar yadda suke gudanar da aikin su.
Wannan murabus din ta haifar da mahawara mai zafi a ciki da wajen jihar Kano, tare da hudubobi a Masallatan Juma’a dangane da muhimmancin hukumar da kuma rawar da take takawa.
Nasirudeen Muhammed zai jagoranci shirin.
Sat, 02 Mar 2024 - 434 - Jana'izar ma'aikacin RFI Hausa, Mahammane Salissou Hamissou a garin Tsibirin Gobir
A jiya Juma'a 17 ga watan Fabrairun 2024 ne aka gudanar da jana'izar ma'aikacin RFI Hausa, Mahammane Salissou Hamissou a garin Tsibirin Gobir, Mahammane Salissou Hamissou wanda Allah Ya yi wa rasuwa a ranar Larabar da ta gabata sakamakon hatsarin mota da ya rutsa da shi a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya.
Sat, 17 Feb 2024 - 433 - Matakin hadin gwiwar da Nijar ,Mali da Burkina Faso suka dauka, na sanar da ficewa daga ECOWAS
Daga cikin muhimman labarun makon jiya da shirin ya sake waiwaya domin bitarsu akwai, matakin hadin gwiwar da Nijar da Mali da kuma Burkina Faso suka dauka, na sanar da ficewa daga kungiyar ECOWAS.
Sai kuma sake karya darajar Naira da gwamnatin Najeriya ta yi, karo na biyu cikin watanni 8.
A Turai kuwa, za a ji yadda zanga-zangar manoma ta bazu zuwa sassan nahiyar saboda adawa da wasu sauye-sauyen mahukuntan kasashen yankin da suka ce ba za su lamunta ba.
Sat, 03 Feb 2024 - 432 - Taron Shugabannin arewacin Najeriya don lalubo hanyar magance matsalar tsaronSat, 27 Jan 2024
- 431 - Rikici tsakanin 'yan ta'adda a arewacin Najeriya ya illata bangaren Dogo Gide
Shirin wannan makon zai fara ne da waiwayar bata-kashin da aka yi tsakanin ‘yan bindiga a Najeriya, lamarin da ya kai ga illata bangaren daya daga cikin jagoran ‘yan ta’adddan da ya addabi jama’a.
Fira Ministan Jamhuriyar Nijar ya yi tatttaki zuwa Iran, bayan ganawarsa da mahukuntan kasar Rasha inda suka karfafa yarjejeniyar tsaron da suka kullla.
A gabashin Afirka kuwa cibi ne ya zama kari, domin kuwa gwamnatin sojin Sudan ce ta katse alaka da kungiyar kasashen yankin gabashin nahiyar ta Afirka, saboda gayyatar shugaba kuma Janar Abdel Fattah al-Burhan da suka yi.
Sat, 20 Jan 2024 - 430 - Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da nasarar Abba Gida-Gida a zaben gwamnan Kano
Cikin shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan makon tare da Nura Ado Suleiman, ya fara ne daga Kano a Najeriya, inda a ranar Juma’ar da ta gabata, kotun koli ta tabbatar da gwamna Abba Kabir Yusuf Abba na jam’iyyar NNPP a matsayin halastaccen gwamnan jihar.
Shirin ya kuma sake waiwayar matakin jagoran mulkin Sojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan na gindaya sharudda gabanin amincewa da shiga tattaunawa da bangaren jagoran dakarun RSF Mohamed Hamdan Dagalo da suka shafe fiye da watanni 9 suna gwabza yaki.
Mon, 15 Jan 2024 - 429 - Gwamnatin Najeriya ta haramta karbar shaidar karatun digiri daga Benin da Togo
Daga cikin labarun da shirin 'Mu Zagaya Duniya' ya sake waiwaya a wannan makon akwai matakin da gwamnatin Najeriya ta dauka na haramta karbar takardun shaidar kammala karatun digiri daga jami'o'in Jamhuriyar Benin da kuma kasar Togo.
Shirin ya kuma leka yankin Gabas ta Tsakiya, inda aka kashe kusan mutane 100 a wani harin ta'addanci da aka kai a kasar Iran.
Mon, 15 Jan 2024 - 428 - Bitar wasu muhimman labaran da suka faru a duniya cikin wannan mako
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai batun yadda yan ta'adda a Najeriya ke gina ramu suna boyewa, saboda barin wutar da suke sha daga sojojin kasar, sai kuma batun kammala ficewar sojojin Faransa a Nijer da dai sauran manyan labaran da suka hada da Burkina Faso, jamhuriyar Benin, yakin Isra'ila da Hamas, tare da dokar yan ci rani da Faransa ta amince da ita.
Sat, 23 Dec 2023 - 427 - ECOWAS/CEDEAO ta tabbatar da juyin mulki aka yi a Nijar
Daga cikin labarun da Shirin ya kunsa akwai matakin da kungiyar kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ko CEDAEO ta dauka na amincewa da da cewar an yi juyin Mulki a Nijar, sannan kuma ta dakatar da ita daga cikin ta har sai lokacin da sojoji suka maida wa farar hula Mulki.
A Najeriya kuma, Bankin Duniya ne ya bukaci gwamnatin kasar ta fadada tsauraran matakan da take dauka na yi wa tattalin arzikin kasar garambawul, domin ceto shi daga durkushewa baki daya a nan gaba.
Sat, 16 Dec 2023 - 426 - COP28 - An samar da asusun tallafa wa kasashe don yaki da matsalar sauyin yanayi
Shirin "Mu zagaya duniya" na wannan makon tare da Khamis Saleh ya waiwari babban taron sauyin yanayi na COP28 da aka faro a Dubai, inda aka samar da wani asusu na musamman da manyan kasashe za su rinka zuba kudi don taimaka kananan kasashen da matsalar da ba su suka samar ba ta fi shafa.
Haka nan shirin ya kuma duba matakin da gwamnatin sojin Nijar ta dauka na dakatar da dokar hana safaran bakin haure, matakin da EU ke ganin a matsayin wata barazana ta kara yawan bakin hauren da zasu kwarara kasashenta.
Ku latsa a lamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh......
Sat, 02 Dec 2023 - 425 - Bitar wasu daga cikin labaran da suka dauki hankali na mako
Shirin zai kuma waiwayi kalaman da tsohon shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo yayi kan cewa Dimokaradiyar kasashen yammacin turai fa ba ta haifa wa nahiyar Afirka da mai idanu ba.
Cikin makon da ya gabata, aka shiga rudani, yayin da kuma a gefe guda aka yi ta tafka muhawara a Kano dake arewacin Najeriya, bayan da kotun daukaka kara ta fitar da takardar hukuncin da ta yanke kan shari’ar zaben gwamnan jihar a juma’ar waccan makon da ya gabata, inda ta tabbatar da hukuncin kotun sauraren kararrakin zabe.
Sai ku biyo mu..............
Sat, 25 Nov 2023 - 424 - MU zagaya Duniya: Kotun daukaka kara a Najeriya ta soke zaben gwamnan jihar Kano
Ciki Shirin wannan makon za a ji cewar Kotun Daukaka karar Najeriya ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben Kano da ya karbe kujerar Gwamnan jihar daga hannunn Abba Kabir Yusuf na NNPP ya mika ta zuwa Nasir Yusuf Gawuna na APC.
Kasar Ghana ta bukaci hadin gwiwar kasashen Afirka domin tilasta wa kasashen da suka yi wa nahiyar mulkin mallaka biyansu diyya akan yadda suka azabtar da su da cinikin bayi.
A Gabas ta tsakiya kuwa Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ne ya zargi mayakan Hamas da dakile duk wani yunkuri na takaita yawan rayukan fararen hular da suke salwanta a Zirin Gaza.
Sat, 18 Nov 2023 - 423 - wasu daga cikin muhimman lamurran da suka wakana a wannan makonSat, 11 Nov 2023
- 422 - Isra’ila ta kashe Falasdinawa sama da dubu 9,000, fiye da rabinsu kuma mata ne da kananan yara
Majalisar Dinkin Duniya, ta bukaci a gaggauta tsagaita wuta a Zirin Gaza, tare da gargadin cewa lokaci na kurewa kasashe kan bukatar dakile yi wa Falasdinawa kisan kare dangi a yankin na Gaza.
Shugaban Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya, Filpipo Grandi ya bukaci mambobin Kwamitin Tsaro na Majalisar da su kawo karshen rarrabuwar kawunan da ke tsakaninsu, don tabbatar da an tsagaita wutar da za ta dakatar da salwantar rayukan Falasdinawa a Zirin Gaza.
Sat, 04 Nov 2023 - 421 - Muhimman labarun lamurran da suka wakana a cikin makoSat, 28 Oct 2023
- 420 - Harin asibitin Gaza ya janyo cece-ku-ce
Cikin labarun da shirin makon nan ya waiwaya akwai Harin da ya kashe daruruwan mutane a babban asibitin Zirin Gaza, lamarin da fusata kasashe da dama, da hukumomi, da kungiyoyin na kasa da kasa, da sauran al’umma a sassan duniya. Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta sanar da dakile wani yunkurin hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum na tserewa daga gidan da ake tsare da shi.
Sat, 21 Oct 2023 - 419 - Halin da ake ciki a Zirin Gaza bayan barkewar yaki tsakanin Isra'ila da Hamas
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' da ya saba waiwayar labarun makon da ya kare a wannan karon ya mayar da hankali kan yakin da ya barke tsakanin Isra'ila da mayakan Falasdinawa na kungiyar Hamas.
Za kuma a ji yadda dubban jama’a suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a sassan duniya, yayin da Amurka ta jaddada goyon bayanta ga Isra’ila.
Sat, 14 Oct 2023
Podcasts similar to Mu Zagaya Duniya
- Global News Podcast BBC World Service
- El Partidazo de COPE COPE
- Herrera en COPE COPE
- The Dan Bongino Show Cumulus Podcast Network | Dan Bongino
- Es la Mañana de Federico esRadio
- La Noche de Dieter esRadio
- Curiosidades de la Historia National Geographic National Geographic España
- Dateline NBC NBC News
- 財經一路發 News98
- La rosa de los vientos OndaCero
- Más de uno OndaCero
- La Zanzara Radio 24
- L'Heure Du Crime RTL
- El Larguero SER Podcast
- Nadie Sabe Nada SER Podcast
- SER Historia SER Podcast
- Todo Concostrina SER Podcast
- 安住紳一郎の日曜天国 TBS RADIO
- アンガールズのジャンピン[オールナイトニッポンPODCAST] ニッポン放送
- 辛坊治郎 ズーム そこまで言うか! ニッポン放送
- 飯田浩司のOK! Cozy up! Podcast ニッポン放送
- 吳淡如人生實用商學院 吳淡如
- 武田鉄矢・今朝の三枚おろし 文化放送PodcastQR
Other News & Politics Podcasts
- Les Grosses Têtes RTL
- Hondelatte Raconte - Christophe Hondelatte Europe 1
- Laurent Gerra RTL
- C dans l'air France Télévisions
- L'œil de Philippe Caverivière RTL
- Enquêtes criminelles RTL
- Bercoff dans tous ses états Sud Radio
- L’heure du crime : les archives de Jacques Pradel RTL
- Hondelatte Raconte - Cote B Europe 1
- Gaspard Proust - Les signatures d'Europe 1 Europe 1
- Les récits de Stéphane Bern Europe 1
- LEGEND Guillaume Pley
- Lenglet-Co and You RTL
- Face à Philippe de Villiers Europe1
- Les chroniques d'Arnaud Demanche RMC
- Fifty States — un Podcast Quotidien Quotidien
- Géopolitique RFI
- RTL Matin RTL
- Apolline Matin RMC
- L'Heure des Pros CNEWS